• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Thursday, May 14, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Ba a kan Ummi Rahab ne Zango ya fara yaudarar ‘yanmata ba – Ali Artwork

by DAGA MUHAMMAD LAWAN RANO
August 24, 2021
in Labarai
0
Ba a kan Ummi Rahab ne Zango ya fara yaudarar ‘yanmata ba – Ali Artwork
0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

FITACCEN jarumin barkwanci, Ali Artwork (Maɗagwal) ya bayyana cewa Adam A. Zango ya daɗe ya na yaudarar ‘yanmata, ba Ummi Rahab ce farau ba.

Haka kuma ya ce yanzu duniya ta gane cewa ashe shi Zango shi ne butulu, ba Rahab ba.

Maɗagwal ya faɗi haka ne a wani rubutu da ya yi bayan ya tura wani bayanin bidiyo na mariƙin Rahab, wato Yasir M. Ahmad.

A ‘yan kwanakin nan dai ana ta ce-ce-ku-ce a tsakanin jarumi Adam Zango da magoya bayan sa a ɓangare ɗaya da kuma Rahab da magoya bayan ta a ɗaya ɓangaren. 

A hirarraki biyu da aka yi da shi ta hanyar bidiyo, waɗanda aka watsa ta hanyar soshiyal midiya, Zango ya bayyana cewa ya raba hanya da jarumar ne lokacin da ta ƙi bin turbar tarbiyya da ya ɗora ta a kai, sannan su kuma magoya bayan sa sun bayyana yarinyar a matsayin butulu wadda ta juya masa baya ta koma wajen maƙiyan sa.

Maɗagwal, wanda aminin Yasir ne, ya wallafa wani bidiyo inda Yasir ɗin ya yi wa duniya bayani kan abin da ya kira gaskiyar abin da ya faru tsakanin jarumar da jarumin.

 A ƙasan bidiyon, Maɗagwal ya yi bayani mai kaushi inda ya ce yanzu gaskiya ta bayyana daga bayanin da Yasir ya yi.

Ya fara da cewa, “Inna lillahi wa inna ilaihir raju’un! To jama’a kun dai ji gaskiyar magana daga bakin ɗan’uwan Ummi Rahab, wato Yasir Rahab. Allah ya kyauta.”

Ya ci gaba da cewa, “Da ma Musulunci ya ce duk abin da za kai, ka yi bincike, kar ka yi saurin yanke wa ɓangare ɗaya hukunci. Shi ya sa mu ka ce jama’a ku yi bincike a kan wannan lamari; ita fa gaskiya guda ɗaya ce, daga ƙin ta sai ɓata. Allah ka dauwamar da mu a kan tafarkin gaskiya.”

Ali Artwork tare da maigidan sa, Injiniya Rabi’u Musa Kwankwaso

Ya ƙara da cewa, “Allah sarki Ummi Rahab! An so a yi miki shigo-shigo ba zurfi, amma Allah ya tsare ki, shi ne ake son a fake da kin yi butulci ko kuma ba kya jin magana.”

Ya ce da man Zango ya saba irin wannan ɓatawar da yaran kamfanin sa, musamman matan.

Ya ce, “Jama’a ina so ku sani, wannan mutumin ba a kan wannan yarinyar ya fara yaudara ba. Ya yi wa mata da dama haka. Don haka in ba za ku manta ba, wannan mutumin ya yi rigima da mata da dama a wannan masana’anta, daga ƙarshe sai ya ce sun masa butulci saboda kawai ya nema bai samu ba. 

“Daga ƙarshe sai ya yi amfani da makafin masoyan sa ta ƙarfin tsiya sai sun dawo mai da yarinyar gurin sa don kawai ya cutar musu da ‘yar marainiyar Allah don ya cimma wata mummunar manufar sa.

“Ku kuma masoyan sa ba ku san me ya ke faruwa ba sai ku yi ta goya masa baya ya na jin daɗi. 

“Yanzu kai da ƙanwar ka ko ‘yar’uwar ka aka yi wa haka, za ka ji daɗi? Kawai a zo soshiyal midiya, ba ta san hawa ba ba ta san sauka ba, a ce ta yi butulci? A sa mutane su yi ta zagin ta da la’anta, ba ta ji ba ba ta gani ba, ‘yar ƙaramar yarinya da ba ta san komai ba wai a ce ta bijire!

“Hakan na nufin ta tafi karuwanci kenan, alhali kuma yarinya babu inda ta ke zuwa daga gida sai gun aikin ta? Wannan ba daidai ba ne, a ɓata sunan ‘yar da duk mai son ta ya aure ta zai fara mata kallon ta na zuwa yawon bariki.”

Da ya juya kan Zango, sai ya ce, “Ka ce za ka aure ta, ka gudu ka ƙi komawa. Wanda su ke son ta tsakani da Allah ka sa musu shakku a kan ta. Shi kenan ka na son ka hana ta aure ko? Ƙaramar yarinya a sa mutane su tsane ta babu gaira babu dalili.”

A cewar Ali Artwork, “Ya kamata ‘yan’uwa mu ji tsoron Allah, mu guji yaɗa ji-ta-ji-ta. Allah ma ya hana haka. 

Aliyu Muhammad Idris (Artwork)

“Kuma in-sha Allah wannan yarinyar za mu ci gaba da yi mata addu’a.”

A ƙarshe, jarumin ya yi addu’a kamar haka: “In-sha Allah ba zai ƙara yi wa wata ‘ya mace haka ba. Don haka mu na ƙara addu’ar Allah ya ƙara tsare miki mutuncin ki, Ummi Rahab. Allah ya ba ki miji nagari ki yi auren ki ki zauna.”

Loading

Tags: Adam A. ZangoAli Artworkhausa filmsKannywoodMadagwalUmmi RahabYasir M. Ahmad
Previous Post

Hisbah ta Kano ta shiga farautar Ummah Shehu

Next Post

‘Yan Kannywood sun yi tir da kalaman Ummah Shehu

Related Posts

Rasuwar dattijon Kannywood, Nura Shareef, ta girgiza ‘yan fim
Labarai

Rasuwar dattijon Kannywood, Nura Shareef, ta girgiza ‘yan fim

February 22, 2026
Daraktar fim ta ƙi karɓar awad saboda kisan gillar da Isra’ila take yi a Gaza
Labarai

Daraktar fim ta ƙi karɓar awad saboda kisan gillar da Isra’ila take yi a Gaza

February 21, 2026
Fitaccen furodusa Kunle Afolayan ya yi haɗin gwiwa da Jamhuriyar Benin kan shirya finafinai
Labarai

Fitaccen furodusa Kunle Afolayan ya yi haɗin gwiwa da Jamhuriyar Benin kan shirya finafinai

February 19, 2026
An naɗa Farfesa Tengya matsayin sabon shugaban Cibiyar Koyon Finafinai ta Ƙasa
Labarai

An naɗa Farfesa Tengya matsayin sabon shugaban Cibiyar Koyon Finafinai ta Ƙasa

February 15, 2026
Alƙali ya ci Samha Inuwa tara ko ta je kurkuku wata 6
Labarai

Alƙali ya ci Samha Inuwa tara ko ta je kurkuku wata 6

February 13, 2026
Hukumar EFCC ta kama jarumar Kannywood, Samha Inuwa, saboda goge majina da takardun naira
Labarai

Hukumar EFCC ta kama jarumar Kannywood, Samha Inuwa, saboda goge majina da takardun naira

February 3, 2026
Next Post
‘Yan Kannywood sun yi tir da kalaman Ummah Shehu

'Yan Kannywood sun yi tir da kalaman Ummah Shehu

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!