• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Monday, August 24, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Ba abin da marigayiya Rabi’atu S. Haruna ta fi so kamar yabon Annabi, inji mijin ta

by DAGA ABBA MUHAMMAD
March 16, 2021
in Labarai
1
Ba abin da marigayiya Rabi’atu S. Haruna ta fi so kamar yabon Annabi, inji mijin ta
0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

MIJIN fitacciyar mawaƙiyar Manzon Allah (s.a.w.), marigayiya Rabi’atu S. Harun, ya bayyana cewa ba abin da matar tasa ta fi so ta riƙa yi kamar yabon Manzon Allah.


Alhaji Shariff Mu’azu, wanda shi ma sha’iri ne, ya faɗa wa mujallar Fim cewa hakan ne ma ya sanya ba ta ce masa ta na so ta yi aikin albashi ba duk da yake ta na da ilimin addini da na boko.


Rabi’atu ta rasu ne da misalin ƙarfe 3:30 na yamma a gidan mijin ta da ke layin Ɗangaladima a Titin Abuja, unguwar Rigasa, Kaduna, a yau Talata, 16 ga Maris, 2021.


Shekarun ta 35 a duniya.


An yi jana’izar ta aka kai ta gidan ta na gaskiya a maƙabartar unguwar Hayin Ɗanmani.


Ita ce ta rera fitattun waƙoƙin nan masu taken ‘Sayyadin Nasi Karimi’ da ‘Mai Daraja Annabi Ma’aiki Gata Na’ waɗanda su ka yi tashe a shekarun baya.

An taru za a yi wa Rabi’atu S. Harun sallah


Mijin ta, Alhaji Shariff Mu’azu, ya shaida wa mujallar Fim cewa marigayiyar ta yi rashin lafiya na tsawon mako biyu, amma ta samu sauƙi kafin ciwon ya dawo.

Sayyada Rabi’atu ta rasu ta bar mijin ta da ‘ya’ya biyu, Ahmad da Khausar.


Da wakilin mujallar Fim ya tambayi mijin abin da zai iya cewa game da wannan babban rashi da ya yi, sai ya ce, “Gaskiya na yi rashi. Domin ta na da kirki, kuma ta na yabon Manzon Allah, don ba ta da wani buri a rayuwar ta da ya wuce wannan yabon, kuma da ya ke ni ma layi na ne sai na bar ta ta ci-gaba da yi.


“Ka ga kuma ta yi karatun boko daidai gwargwado, sannan ta yi karatun addini, don har Larabci ma ta na ji, amma ba ta taɓa nuna min ko za ta yi wani kasuwanci ko wani aikin gwamnati haka ba, sai dai yabon Annabi S.A.W. kawai, shi ya sa ni kuma na ƙarfafa mata gwiwa na ba ta dama ta ci gaba. 

An kawo Rabi’atu S. Harun bakin kabarin ta


“Ni yanzu babu abin da zan ce sai dai fatan Allah ya jiƙan ta da rahama. Allah ya sada ta da Annabin Muhammadu s.a.w.”


Allahu Akbar! Da ma Allah ya ce dukkan mai rai sai ya ɗanɗani mutuwa. 


Labarin mutuwar Rabi’atu ya girgiza farfajiyar mawaƙan begen Annabi Muhammad (SAW) da ma sauran jama’a. Labarin ya yaɗu a soshiyal midiya jim kaɗan da rasuwar, kuma duk wanda ya karanta labarin sai ya kaɗu kuma ya yi mata addu’a.

Mu ma a mujallar Fim mu na addu’ar Allah ya jiƙan Rabi’atu S. Harun da rahama, ya kuma albarkaci dukkan abin da ta bari, amin.

Ana rufe Rabi’atu S. Harun
Allahu Akbar! Wannan ita ce kushewar masoyiyar Manzon Allah, Rabi’atu S. Harun, jim kaɗan bayan an rufe ta
Previous Post

Na sha gamuwa da masu sha’awa ta – Nafisa Salisu, jarumar ‘Macen Sirri’

Next Post

Gwamnati ta taskace ‘yan Nijeriya miliyan 30 a Rajistar Al’umma ta Ƙasa

Related Posts

Mutuwar aure na ƙaddara ce – Jaruma Khadija Yobe
Labarai

Mutuwar aure na ƙaddara ce – Jaruma Khadija Yobe

August 23, 2026
Aina’u Ade ta raba wa tsofaffin jaruman Kannywood tallafin kuɗi
Labarai

Aina’u Ade ta raba wa tsofaffin jaruman Kannywood tallafin kuɗi

August 23, 2026
Ƙungiyar ‘Triple R Kannywood’ ta ziyarci jarumi Tanimu Akawu a asibiti
Labarai

Ƙungiyar ‘Triple R Kannywood’ ta ziyarci jarumi Tanimu Akawu a asibiti

August 23, 2026
Ƙungiyar Triple R ta ba jarumin Kannywood Mustapha Musty tallafin N500,000
Labarai

Ƙungiyar Triple R ta ba jarumin Kannywood Mustapha Musty tallafin N500,000

August 18, 2026
Yadda na gamu da ibtila’in karaya a ƙafa – Jarumi Ɗan’azumi Kamaye
Labarai

Yadda na gamu da ibtila’in karaya a ƙafa – Jarumi Ɗan’azumi Kamaye

August 14, 2026
Tozali TV zai yi bikin Henna Ball da karrama masu ƙwazo da tallafa wa waɗanda suka tsira daga hare-hare a ranar 31 ga Oktoba
Labarai

Tozali TV zai yi bikin Henna Ball da karrama masu ƙwazo da tallafa wa waɗanda suka tsira daga hare-hare a ranar 31 ga Oktoba

August 8, 2026
Next Post
Gwamnati ta taskace ‘yan Nijeriya miliyan 30 a Rajistar Al’umma ta Ƙasa

Gwamnati ta taskace 'yan Nijeriya miliyan 30 a Rajistar Al'umma ta Ƙasa

Comments 1

  1. Hajiya ladidi says:
    5 years ago

    Allah ya gafarta Mata

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!