SHAHARARREN jarumi kuma mawaƙi a masana’antar Kannywood, Adam A. Zango, ya bayyana cewa rashin kai zuciya nesa da kau da ido har ma da rashin tawakkali ne ke sanya matasa faɗawa harkokin da ba su kamata ba a wannan zamani.
A cewar sa, matasan wannan zamani za su iya komai musamman idan su ka taso a cikin halin matsi wanda zai iya kai su ga samun ribar abokai wajen sanya su cikin wani hali na Allah-wadai.
Jarumin ya bayyana haka ne a daren jiya Alhamis, 24 ga Satumba, 2021 bayan wani taron nuna wani sabon fim mai suna ‘Ribar Duniya’ wanda aka shirya wa ‘yan jarida a gidan sinima na Platinum da ke Kano, kafin a fara haska fim ɗin a sinima.
Kamfanin shirya finafinai na ‘Shehu Media Entertaiment’ ne ya shirya fim ɗin.
Da ya ke jawabi ga manema labarai, Zango, wanda shi ne jarumin fim ɗin da ya fito a matsayin Sardauna, ya yi tsokaci musamman ga rayuwar matasa a yanzu.
Ya ce, “Matashi a wannan lokaci zai taso ba shi da kuɗi kuma ba zai gode wa Allah ba, sai ya yi ta tunanin ta wace hanya zai bi domin ya ga ya samu kuɗi.
“Matasan yanzu za su iya bin kowace hanya ta samun kuɗi kuma wannan dalilin ya sa ake samun mutane a cikin sana’o’i irin su damfara, kidinafin, sace-sace, kashe mutane, shiga ƙungiyar asiri da sauran su idan har mutum ba shi da tawakkali ko kuma bai yarda da Allah ne ya ke arziki ko ya ke hanawa ba. To idan mutum bai yarda da wannan ba, mutum zai iya faɗawa kowanne hali.”
Zango ya ba matasa shawara da cewa, “Duk wani matashi ya kamata ya nemi na kan sa, kar ya tsaya hangen wani wanda ya ke wucewa da motoci ko ya dinga hangen wani da ya ke riƙe manyan wayoyi ko hangen wani da kayan alfarma ya yi tunanin cewa shi ma gobe sai ya samu. Bai san yadda wannan mutumin ya yi ya mallaki waɗannan abubuwan ba. Ta yiwu ta hanyar da ya dace ne ko kuma ta akasin haka.
“Don haka matasa mu daina kallon wani mu ce za mu zama irin shi ba tare da mun dogara da Allah ba.”
Shugaban kamfanin da ya ɗauki nauyin wannan fim, Alhaji Shehu Mika’ilu Abdullahi, ya bayyana dalilin da sa ya shirya fim ɗin. Ya ce, “Ko da yake wannan fim ɗin shi ne farkon aiki na, da man na daɗe ina ta tunanin ya za a yi na zo industiri.
“Kuma da man ina da sha’awar wannan aiki a Kannywood, to kuma Allah ya kawo wannan lokacin, don mun daɗe mun a shirya yadda za a yi mu shirya wannan fim ɗin, sai Allah ya kawo wannan lokacin.
“Kuma wannan shi ne aiki na na farko kuma ina da burin ci gaba da shirya wasu finafinan.
“Mun shirya wannan fim ne saboda yanayin abubuwan da ke faruwa a cikin al’ummar mu. Mu na neman labari wanda zai wa’azantar da mutane yanzu, kuma abu ne yanzu da mutane ya kamata su guda kamar yadda rayuwa ta ke kasancewa a yanzu saboda in kun duba samari a yanzu irin manyan wayoyin da su ke riƙewa abin kai za su iya komai don su samu dukiya.
“To wannan fim ya na daga cikin abubuwan da ya kamata mutane su ga ne.”
Alhaji Shehu ya ce duk da yake shi sabon shiga ne a wannan masana’anta, ya samu wani ilimi a yayin ɗaukar fim ɗin, musamman ma yadda ake haƙuri da jama’a.
Ya ce, “Darasin da na samu yayin ɗaukar wannan fim shi ne haƙuri; kar mutum ya yi gaggawar yin wani abu. A dinga haƙuri saboda ba mu san yadda rayuwa za ta kasance ba.”
Ya kuma yi kira ga jama’a da su je su kalli wannan fim don irin darasin da ya zo da shi.
A taron, an ba ‘yan jarida da jaruman fim ɗin dama su fara kallon fim ɗin kafin a sake shi ga jama’ar gari don su bayyana gyara da shawarwari ga waɗanda su ka shirya shi.
‘Ribar Duniya’ fim ne da aka shirya don a tura wa masu kallo saƙo kan yadda duniya ta koma a yau inda mai dukiya ke samun abu cikin kwanciyar hankali in ya yi amfani da kuɗin sa, yayin da wanda bai da shi ba a ma kulawa da shi.
Fim ɗin ya kuma nuna irin illar yadda aka yi watsi da al’adar bincike kafin aure, musamman idan auren ya zo da abin duniya, da kuma nuna illar rabuwa da wanda ya kamata mace ta aura, wato wanda ya ke da dangi da aka san su, da sauran illolin da ya kamata Hausawa su duba don su gyara.
Ya ƙunshi jarumai irin su Adam A. Zango, Abdul M. Shareef, Fatima Hamisu, Rabi’u Rikadawa, Fati S.U., da sauran su.
Malam Alhassan Toron Giwa ne ya rubuta labarin wannan fim kuma Alfazazee Muhammad ya bada umarni.
Tuni dai aka fara haska fim ɗin a gidan sinima na Platinum da ke birnin Kano.