MAWAƘI Nazifi Asnanic ya shiga tsaka mai wuya sakamakon jin sunan sa da aka yi a cikin waɗanda ake tuhuma da tarzomar siyasa a garin Tudun Wada da ke Jihar Kano a ranar Laraba da ta gabata.
A rikicin, an ba da labarin an kai hari a ofishin jam’iyyar NNPP a garin har aka ƙone mutum sama 10 har lahira, kuma ‘yan sanda sun ba da tabbacin kama wanda ake zargi da jagorancin kai harin, wato ɗan Majalisar Wakilai Alhassan Ado Doguwa, tare da ‘yan bangar siyasar sa, kuma an gurfanar da su a gaban kotu a ranar Laraba.
A cikin waɗanda ake tuhuma ɗin an samu wani mai suna Nazifi Asnanic a lokacin karanto tuhumar da ake yi masu. Jin wannan sunan ya jefa mawaƙi Asnanic
cikin jimami.
Tun daga lokacin da labarin zaman kotun ya bazu a gari mutane su ke ta tambayar me ya kai Nazifi Asnanic cikin ‘yan bangar siyasa a matsayin sa na mawaƙi?
Sai a wata tattaunawa da mujallar Fim im ta yi da shi ta waya, mawaƙin ya ce: “Faruwar lamarin da kuma yadda labarin ya yaɗu ya tayar mana da hankali da ni da iyalai na. Saboda mutane su na ta kira na tare da tambayar duk wani na kusa da ni a kan yadda suna na ya fito a cikin su.”
Asnanic ya ce: “Mutane su kwantar da hankalin su, ba ni Nazifi Asnanic da su ka sani ba ne. Sunan mu ne ya zo ɗaya, amma dai ba ni da wata alaƙa da waɗancan mutane da aka gurfanar a kotu bisa zargin abin da ya faru na ƙone mutane a garin Tudun Wada.”