• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Wednesday, May 6, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Hirar mujallar Fim da Maryam Yahaya da mahaifin ta kan rashin lafiyar ta

by DAGA MUHAMMAD LAWAN RANO
July 26, 2021
in Labarai
10
Hirar mujallar Fim da Maryam Yahaya da mahaifin ta kan rashin lafiyar ta
0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram


* Sun ƙaryata raɗe-raɗin wai jifar ta aka yi

* Mun bar wa Allah komai, inji su

FITACCIYAR jarumar Kannywood Maryam Yahaya da iyayen ta sun ƙaryata ji-ta-ji-tar da ake yaɗawa cewa wai an yi mata makaru ne wanda ya sa ta ke fama da rashin lafiya a yanzu.

Sun bayyana haka ne a wata ganawa ta musamman da su ka yi da mujallar Fim a daren yau.

Tun da aka wayi gari a yau dai aka dinga yaɗa labarin cewa jarumar ta na fama da tsananin rashin lafiya, musamman ma a soshiyal midiya inda kowa ke ta faɗin abin da ya ga dama a kan lamarin, har wasu na cewa jarumar ta mutu.

To sai dai jarumar ta ce ba haka labarin ya ke ba.

A lokacin da wakilin mu ya kai ziyarar gani da ido a gidan iyayen Maryam a Kano domin gano gaskiyar surutan da ake bazawa a faɗin ƙasar nan game da ita, mahaifiyar jarumar ta yi masa iso zuwa wurin jarumar.

Wakilin namu ya yi kaciɓus da jarumar da ‘yan’uwa da abokan arziki su na ta hira, sun sa Maryam a tsakiya, wanda hakan alama ce ta ta na samun sauƙi.

A tattaunawar ta da mujallar Fim, Maryam Yahaya ta bayyana mamaki kan yadda ake ta surutu a kan abin da ba a tabbatar ba ko aka je aka gani ba.

Jarumar ta ce, “Kamar kowane ɗan’adam Allah ya na jarabtar sa da cututtuka, ni ma ya jarabce ni a wannan lokaci. Amma ni na san cewa komai ya na da lokaci, sai dai masu yin yamaɗiɗi.”

Da mujallar Fim ta tambaye ta ainihin abin da ya ke damun ta, sai ta ce, “Kawai dai cuta ce daga Allah.”

Maryam Yahaya

A kan ji-ta-ji-tar da ake yaɗawa cewa wai wasu daga cikin abokan sana’ar ta ne su ka yi mata asiri, Maryam ta ƙaryata batun da cewa, “Ni na san Allah ne ya ɗoro min, kuma ba na zargin kowa a cikin wannan masana’anta. 

“Hasali ma dai, mu na zaune da kowa lafiya domin jarumai sun zo duba ni da dama; wasu na sani, wasu ma ban sani ba ina kwance. Ba abin da zan ce da Allah sai godiya bisa ni’imar sa.”

Da mujallar Fim ta tambayi jarumar ko ta na samun tallafi daga abokan sana’ar ta ‘yan fim, sai ta amsa da cewa, “Ina samu, sosai ma, domin duk wanda ya zo za ka ga ya kawo mani wani abu, da sauran su. Su na hidima da ni sosai.”

Ta kuma miƙa saƙo ga masoyan ta da cewa, “Ina samun sauƙi kuma ban mutu ba kamar yadda wasu ke yaɗawa, sai dai kawai yanzu ba na jin ƙarfin jiki na; kun san dai marasa lafiya kan ya dawo daidai.”

Bayan tattaunawa ta Maryam, wakilin mu ya ji ta bakin mahaifin ta, Malam Yahaya Yusuf, wanda ya bayyana cewa sun ɗauki kwanaki wajen 40 su na ɗawainiya da rashin lafiyar jarumar.

Ya ƙara da cewa kowa Allah ya kan iya jarabtar sa a kan komai.

A kan raɗe-raɗin da ake yi, malamin ya ce, “Ba ma alaƙanta wannan abu da sa hannun wani. Allah ne ya kawo, kuma shi zai yaye. Na gode.”

A lokacin wannan ziyara, wakilin mu ya lura da cewa Maryam ta rame sosai, domin kuwa duk wanda ya san ta a baya to yanzu idan ya ga ramewar da ta yi dole ya tausaya mata.

Rashin lafiyar nata ya kai ga har ba kowa ake bari ya shiga inda ta ke ba don ya duba ta.

Da fatan Allah ya tashi kafaɗun ta, amin.

Loading

Tags: hausa filmsKannywoodMaryam Yahaya
Previous Post

Sai da aka biya N5m kafin ‘yan bindiga su sako ni – furodusa Ali Bulala Gusau

Next Post

Ɓatanci ga Annabi: ‘Yan Kannywood sun yi tir da ‘Sahara Reporters’

Related Posts

Rasuwar dattijon Kannywood, Nura Shareef, ta girgiza ‘yan fim
Labarai

Rasuwar dattijon Kannywood, Nura Shareef, ta girgiza ‘yan fim

February 22, 2026
Daraktar fim ta ƙi karɓar awad saboda kisan gillar da Isra’ila take yi a Gaza
Labarai

Daraktar fim ta ƙi karɓar awad saboda kisan gillar da Isra’ila take yi a Gaza

February 21, 2026
Fitaccen furodusa Kunle Afolayan ya yi haɗin gwiwa da Jamhuriyar Benin kan shirya finafinai
Labarai

Fitaccen furodusa Kunle Afolayan ya yi haɗin gwiwa da Jamhuriyar Benin kan shirya finafinai

February 19, 2026
An naɗa Farfesa Tengya matsayin sabon shugaban Cibiyar Koyon Finafinai ta Ƙasa
Labarai

An naɗa Farfesa Tengya matsayin sabon shugaban Cibiyar Koyon Finafinai ta Ƙasa

February 15, 2026
Alƙali ya ci Samha Inuwa tara ko ta je kurkuku wata 6
Labarai

Alƙali ya ci Samha Inuwa tara ko ta je kurkuku wata 6

February 13, 2026
Hukumar EFCC ta kama jarumar Kannywood, Samha Inuwa, saboda goge majina da takardun naira
Labarai

Hukumar EFCC ta kama jarumar Kannywood, Samha Inuwa, saboda goge majina da takardun naira

February 3, 2026
Next Post
Ɓatanci ga Annabi: ‘Yan Kannywood sun yi tir da ‘Sahara Reporters’

Ɓatanci ga Annabi: 'Yan Kannywood sun yi tir da 'Sahara Reporters'

Comments 10

  1. Rashee Usman says:
    5 years ago

    Rasheedau95@gmail.com

  2. Rashee Usman says:
    5 years ago

    Allah ya bata lfy

  3. Pingback: Masha Allah! Yadda Hirar Maryam Yahaya da mahaifin ta kan rashin lafiyar ta – HausaLoaded.Com
  4. Jaafar Ameenu Awai says:
    5 years ago

    To komadai menene ai ita rashin lafiya tanakan kowa, Kuma Wanda yafi qarfin Allah yajabeshi da cuta, inayimata addua Allah yabata lafiya, da duk sauran wadanda basuda lafiya.

  5. Musa Ubaliyo Nguru says:
    5 years ago

    Allah ya bata lafiya yasa kaffara ne.

  6. Ibrahim Isa Yakubu says:
    5 years ago

    Allah ya bata lafiya ya kuma sa kaffara ce a gareta ya kuma basu ikon cin jarrabawa da ita da iyayen ta.
    Amin.

  7. Naseeb says:
    5 years ago

    Allah ya bata Lafiya, amma Maryam tana da wani Hali na wulakanta mutane masu daraja da mutunci … wani idan ya hakura akan wulakanci wani bazai iya hakura ba.. ba dole sai ta saurari mutum ba amma mutunta mutum a matsayinsa na dan Adam wani abu ne..
    Mutune suna iya yafe Komai amma basa iya yafe wulakanci … wannan shine tsokacina …Allah ya bata lafiya

  8. Mansoor idrees usaini dayawa says:
    5 years ago

    Allah yasa kaffarace ameen (daga sarkin yakin maryam yahaya na jihar katsina kafur LGA DAYAWA YARTALATA)Mansoor m.i.d

  9. Bilyaminu Ibrahim says:
    5 years ago

    Allahu ya bata lafiya yasa kaffara ne.

  10. meenat says:
    5 years ago

    Comment:sunan Allah mai rahma mai jinkai INA rokon Allah sauki kuma muna Neman gafararsa akowane yanayi kuma muna fatar ya amsa mana da alhairansa amin.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!