MATASHIYAR jaruma kuma mawaƙiya Hauwa’u Abubakar (Fulani), wadda aka fi sani da Hauwa Rafin Guza, ita ma ta shiga sahun ‘yan fim waɗanda su ka shigo shekarar 2022 da ƙafar dama, domin kuwa za ta yi aure a ranar Asabar mai zuwa, 29 ga wannan watan na Janairu, 2022.
Za a ɗaura auren ta da sahibin ta, Muhammad Lawal Habeeb (Bala), da misalin ƙarfe 2:00 na rana a gida mai lamba, K12, Titin Fulani da ke unguwar Rafin Guza, Kawo, Kaduna.


Ubangidan ta, darakta Abdullahi Abu Uku, ya shaida wa mujallar Fim cewa tun a shekarar da ta gabata ta sanar da shi cewa ta bar industiri saboda za ta yi aure.
Sai dai ba kowa ya san da maganar auren Hauwa Rafin Guza ba sai a yau 25 ga Janairu da su ka fitar da katin auren da kuma hotunan kafin aure, wanda ubangidan nata ya jagoranci tura katin da kuma hotunan.


Abdullahi Abu Uku ya tura katin a soshiyal midiya, inda ya ce bai ɗauke wa kowa halartar ɗaurin auren ba.
Wasu daga cikin finafinan da Hauwa ta fito a cikin su sun haɗa da ‘Autar Mama’, ‘Sauyin Ƙaddara’, ‘Ƙiriniya’, ‘Shalele’, ‘Mata Tara’ da sauran su.

A ɓangaren waƙa kuma, akwai ‘Soyayya Ruwan Zuma’, ‘Tsuntsun Soyayya’, ‘Autar Mama’ da sauran su.
Allah ya bada zaman lafiya.
![]()







