• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Tuesday, June 17, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Yadda Abba Sadau, yayan Rahama Sadau, ya angwance

by DAGA ABBA MUHAMMAD
January 31, 2021
in Ranar Murna
0
Yadda Abba Sadau, yayan Rahama Sadau, ya angwance
0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

RANA ba ta ƙarya, sai dai uwar ɗiya ta ji kunya, a cewar masu iya magana. Kamar yadda mu ka kawo maku hira da mu ka yi da yayan fitacciyar jaruma Rahama Sadau, wato Abba Sadau, game da auren sa, to, Allah ya tabbatar da Zainab Musa Yarima ta zama matar sa.

A ranar Asabar, 30 ga Janairu, 2021 aka ɗaura auren na Abba, wanda cikakken sunan sa Haruna Ibrahim Sadau, da santaleliyar amaryar tasa wadda ake yi wa laƙabi da Zee Yarima.

An ɗaura auren ne a masallacin A’ishatu Ɗan’iyan Misau da ke Titin Shagari, a unguwar Badarawa, Kaduna, a kan sadaki N100,000.

Wasu daga cikin ‘yan fim da su ka halarci ɗaurin auren sun haɗa da Yaseen Auwal, Sanusi Oscar 442, Sani Candy, da Yunusa Mu’azu.

Tun a ranar Alhamis, 28 ga Janairu, aka yi wasan ƙwallon ƙafa a filin wasa na Ahmadu Bello da ke Kaduna, inda aka buga wasa tsakanin ‘yan Kannywood da abokan ango.

Wasu daga cikin waɗanda su ka halarci wasan ƙwallon sun haɗa da Umar M. Shareef, Sadiq Sani Sadiq, Ubalen Danja, da Tukur Musa (TK). TK shi ne ya ɗauki nauyin shirya wasan ƙwallon, inda abokan ango su ka ci ‘yan Kannywood.

Amarya da ango sun iso wajen dina
Rahama Sadau ta na yi wa Ado Gwanja liƙi

Bayan an ɗaura aure, sai aka ɗunguma zuwa gidan cin abinci ɗin nan na Rahama Sadau mai suna ‘Sadauz Home: da ke Titin Raɓah, aka yi walima.


Haka kuma a daren ranar Asabar ɗin, an shirya gagarumar dina a gidan su Abba da ke Titin Jabi, Unguwar Rimi, wadda an yi ta ne a gida sakamakon dokar rashin bada ɗakunan taro da gwamnati ta saka saboda annobar korona.


An saka lokaci za a fara dinar da misalin ƙarfe 8:00 na dare, amma ba a fara ba sai wajen ƙarfe 10:00 na dare. 


‘Yan fim da mawaƙa sun baje kolin su a wurin. 


Mawaƙan da su ka nishaɗantar da taron sun haɗa da Umar M. Shareef, Ado Isah Gwanja, da Usman Umar (Sojaboy). 


A wurin dinar an ware lokaci da aka ba ango da amarya dama su ka yanka kek, su ka ciyar da junan su. 

Ango da abokan sa a wajen dina
Rahama Sadau da mahaifiyar ta

Bayan yanka kek ɗin, ango ya fara ciyar da amarya, sannan ya ba ƙanwar sa Rahama da ƙawayen ta Fati Washa da Maryam Aliyu (Madam Korede) kek ɗin a baki kamar yadda ya ba amaryar sa. 


Iyayen Abba da ƙannen sa su ma ba a bar su a baya ba, domin duk su na wurin dinar, kuma sun yi hotunan nuna ƙauna gwanin ban-sha’awa. 


‘Yan fim da su ka halarci dinar sun haɗa da Falalu A. Ɗorayi, Yaseen Auwal, Usman Umar (Sojaboy), Umar M. Shareef, Yusuf Haruna (Baban Chinedu), Mubarak Umar, Sulaiman Sir Zeesu, Jamilu Away Man, Yunusa Mu’azu, Aminu Mirror, Kabiru Zango, Fati Washa, ZPreety, da Maryam Aliyu (Madam Korede).


Bikin ya ƙayatar da ‘yan kallo matuƙa.


Haka aka tashi kowa na yi wa sababbin ma’auratan fatan Allah ya ba su zaman lafiya da zuri’a ɗayyiba.


A yanzu dai ‘ya’ya mata na gidan Alhaji Ibrahim Sadau waɗanda ake kira ‘Sadau Sisters’ sun tashi daga huɗun da aka sani sun zama biyar, ma’ana Rahama, Zainab, Aisha, Fatima, to kuma da amaryar Abba Sadau, Zainab Musa Yarima Sadau.

Rahama Sadau da jaruma Maryam Aliyu (Madam Korede)
Amarya tare da ƙannen mijin ta. Yanzu ‘Sadau Sisters’ sun zama biyar har da ita!
Amarya da ango tare da iyayen ango
‘Ya’yan Alh. Ibrahim Sadau baki ɗayan su tare da amarya Zainab
Fati Washa (a hagu) tare da Rahama Sadau da ma’auratan a wajen yanka kek
Amarya da ango sun iso wajen dina
Mahaifiyar ango tare da amaryar ɗan ta
Tags: Abba SadauAdo GwanjaAlhaji Ibrahim SadauFati WashaFim MagazineHausa weddingKannywoodMadam KoredeMaryam AliyuRahama SadauSadau SistersZainab Musa Yarima
Previous Post

Mawaƙi Umar Ɗan-Hausa da Fatima Bashir sun angwance

Next Post

Mun daina yafe wa masu satar ‘Izzar So’ – Lawan Ahmad

Related Posts

Jarumin Kannywood, Abdul M. Shareef zai auri jaruma Maryam Malika
Labarai

Jarumin Kannywood, Abdul M. Shareef zai auri jaruma Maryam Malika

June 12, 2025
An ɗaura auren darakta a Kannywood, Al-Amin Ciroma da ‘yar’uwar sa Sharifatu
Ranar Murna

An ɗaura auren darakta a Kannywood, Al-Amin Ciroma da ‘yar’uwar sa Sharifatu

May 2, 2025
Ƙarshen tika-tika, tik! A’ishatulhumaira ta zama matar Rarara ta huɗu
Ranar Murna

Ƙarshen tika-tika, tik! A’ishatulhumaira ta zama matar Rarara ta huɗu

April 25, 2025
Darakta Al-Amin Ciroma zai yi amarya a watan gobe, shekaru biyu bayan mutuwar auren sa da Wasila Isma’il 
Ranar Murna

Darakta Al-Amin Ciroma zai yi amarya a watan gobe, shekaru biyu bayan mutuwar auren sa da Wasila Isma’il 

April 20, 2025
Ahlan tare da 'yar sa Hassana, amaryar mako mai zuwa
Ranar Murna

Jarumi a Kannywood, Ahlan zai aurar da ‘yar sa Hassana

February 16, 2025
Daɗi kan daɗi: Marubuciya Bilkisu Yusuf Ali ta samu jika da digirin digirgir
Ranar Murna

Daɗi kan daɗi: Marubuciya Bilkisu Yusuf Ali ta samu jika da digirin digirgir

December 20, 2024
Next Post
Mun daina yafe wa masu satar ‘Izzar So’ – Lawan Ahmad

Mun daina yafe wa masu satar 'Izzar So' - Lawan Ahmad

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!