A DAREN jiya wani mugun labari ya ɓarke a soshiyal midiya, aka ce wai fitaccen jarumi Sani Garba SK ya rasu.
Wasu gidajen yana da shafukan tattaunawa sun yaɗa labarin wanda ya bazu kamar wutar bazara.
Labarin ya ɗaga hankalin mutane da dama, wasu na ta tambayar idan da gaske ne, yayin da wasu kuma sun gaskata shi.
Babu ruwan irin waɗannan shafukan da bin ƙa’idar aikin jarida ta tabbatar da labari kafin a buga shi, shi ya sa su ke rige-rigen yaɗa labarin ƙanzon kurege, abin da a Turance ake kira ‘fake news’.
Binciken da mujallar Fim ta yi ya gano cewa shafukan labarai da dama a Facebook sun yaɗa ƙirƙiri labarin, ko da yake daga baya wasu sun ƙaryata kan su da kan su.
Sai dai tun a lokacin da labarin ya ɓulla wakilan mu su ka gano cewa shaci-faɗi ne da ƙage.
‘Yan fim da dama sun nuna damuwa kan wannan labarin ƙaryar da aka yaɗa kan Sani SK, wanda ya ke kwance a Asibitin Nassarawa a Kano, ya na karɓar magani.
A makon jiya, a ranar 18 ga Nuwamba, an yaɗa wani guntun bidiyo a soshiyal midiya inda aka ga SK a zaune a kan gadon asibiti, ya na roƙon jama’a da su taimaka masa da kuɗin sayen magani.
Wani aminin majinyacin, fitaccen jarumi Aminu Surajo Bono, ya ɗauki saƙon murya da wayar sa bayan ya zanta da SK a daren jiya, ya tura wa jama’a tare da kira a gare su da su yi watsi da labarin da ake yaɗawa.
Aminu S. Bono ya ce: “Salamu alaikum jama’a. Don Allah duk wanda ya ke maganar S.K. ƙarya ne. Yanzu ma na kai minti biyar ina waya da shi, da wasan mu da dariyar mu yadda mu ka saba da kuma fara’ar sa da komai. Ya na nan a asibiti a ɗakin sa inda ya ke karɓar magani.
“So, duk wanda zai ji wani abu a Facebook don Allah ya je ya yi ‘comment’ ya ƙaryata. Ƙarya ne!”
Mujallar Fim ta tuno da cewa ba a yanzu ba ne aka fara yaɗa labarin ƙarya kan mutuwar wani ɗan fim, domin kuwa tun ma kafin zuwan soshiyal midiya kusan kowane babban jarumi an sha cewa ya rasu.
Zuwan soshiyal midiya ya sanya irin wannan labarin ƙaryar ya fi saurin yaɗuwa, domin kuwa cikin minti kaɗan ya ke bazuwa a sassan duniya.
Jarumai biyu na baya-bayan nan da aka yi ƙaryar cewa ya rasu su ne Malam Sani Idris Kauru (Moɗa) da Alhaji Usman Baba Pategi (Samanja Mazan Fama), waɗanda dukkan su mazauna Kaduna ne.
![]()







