A YANZU haka shirye-shiryen bikin auren ‘yan Kannywood biyu, wato jaruma a shirin ‘Izzar So’, Khadija Yobe, da mawaƙi Izzuddeen M. Doko (Izzu Bawan Allah) sun kankama.
Mujallar Fim ta ruwaito cewa har an fitar da hotunan kafin aure na ma’auratan.

Za a ɗaura auren a ranar Juma’a mai zuwa, wato 10 ga Fabrairu, 2023 a masallacin Juma’a na unguwar Nassarawa da ke garin Damaturu, babban birnin Jihar Yobe, da misalin ƙarfe 2 na rana.
Allah ya kai mu.

![]()






