MAIGARIN Gwagwarwa a Kano, Alhaji Usman Sunusi Aliyu, zai naɗa jarumar Kannywood, Hajiya Hadiza Muhammad (Hadizan Saima) matsayin Tauraruwar Gwagwarwa a jibi Asabar.
Za a yi naɗin a taron da za a yi da safe a Special Primary School, Gwagwarwa, da ke Riga a Unguwar Brigade da ke Ƙaramar Hukumar Nassarawa a cikin garin Kano.
Da wannan naɗin, ita ma Hadizan Saima za ta shiga cikin sahun ‘yan fim masu riƙe da sarautar gargajiya.
Tuni ‘yan’uwa da abokan arziki suka shiga aika mata da saƙon taya murna da fatan Allah ya sa a yi taro lafiya.
![]()







