WATA sabuwar ƙungiyar tafiyar siyasar ‘yan fim mai suna Kannywood Kwankwasiyya ta kai wa Hukumar Tace Finafinai da Ɗab’i ta Jihar Kano Abba El-Mustapha ziyara domin gabatar kan ta da kuma nuna goyon bayan su a ga hukumar bisa manufofi da kuma tsare-tsaren Gwamnatin Abba Kabir Yusuf da jagoran siyasar Kano, Sanata Rabi’u Musa kwankwaso.
‘Yan ƙungiyar sun kai ziyarar a ranar Litinin, inda suka samu kyakkyawar tarba daga Babban Sakataren hukumar, Alhaji Abba El-Mustapha.
A lokacin ziyarar, shugaban ƙungiyar, Alhaji Isma’il Khalil Ja’en Mahy, ya bayyana cewa sun kafa ƙungiyar ne “duba da yadda aka bar Kannywood a baya babu wata ƙungiya da take morar gwamnati da wani abu duk da Kannywood muna da yawa, sannan Kwankwasiyya tana da mabiya da yawa a Kannywood.
“Amma ko a kwanaki Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya taimaki ƙungiyoyi da dama amma babu ƙungiyar Kannywood ko ɗaya a ciki.
“Wannan dalili ya sa muka tabbatar da wannan ƙungiyar da za ta rinƙa tallata ayyukan Gwamna Abba Kabir Yusuf birni da ƙauyuka don wayar da kan al’umma a kan gwamnatin Jihar Kano ƙarƙashin Abba Kabir Yusuf.”

Da yake mayar da jawabi, El-Mustapha ya nuna farin ciki da jin daɗin sa bisa wannan ziyara, sannan ya bayyana ƙungiyar a matsayin wadda ta zo da kyakkyawar manufa.
Shugaban ya ce zai yi iya bakin ƙoƙarin sa wajen taimakon ƙungiyar.
El-Mustapha ya yi jan hankali a kan duk wanda zai bada gudunmawa a harkar Kwankwasiyya a ja shi a jiki a yi tafiyar da shi kuma kada a yi ƙungiya don cin zarafin wasu, ya zama an yi ta ne don samar wa Kannywood cigaba tare da nemo hanyar da gwamnati za ta taimaki ‘yan Kwankwasiyya na Kannywood.
A tawagar ‘yan ƙungiyar Kannywood Kwankwasiyya ɗin dai akwai da Isma’il Khalil Ja’en, Tijjani Faraga, Safiya Kishiya, Yahanasu Sani, Hassana Musa, Mariya Ibrahim, da sauran su.

![]()







