FITACCEN mawaƙin Hausa, Ado Isa Gwanja, yana kwance a asibiti bayan ya kamu da rashin lafiya.
A wata tattaunawa da ya yi da mujallar Fim, ɗan’uwan sa, Alhaji Sa’idu Isa Gwanja, ya bayyana cewa ƙanen nasa ya kamu da rashin lafiyar ne kwanaki biyu da suka gabata, sakamakon kamuwa da zazzaɓin cizon sauro (maleriya), wanda daga bisani ya tsananta.
Ya ce a halin yanzu Ado Gwanja yana karɓar magani a Asibitin Koyarwa na Malam Aminu Kano (AKTH), inda likitoci suke kula da lafiyar sa.
“A yanzu haka muna Asibitin Koyarwa na Malam Aminu Kano, inda yake karɓar magani. Muna roƙon al’umma da masoyan sa da su taya shi da addu’a, domin Allah ya ba shi cikakkiyar lafiya,” inji Sa’idu Isa Gwanja.
Masoya da abokan sana’ar Ado Gwanja suna ci gaba da bayyana fatan alheri tare da yi masa addu’ar samun sauƙi da dawowa bakin aikin sa cikin ƙoshin lafiya.
![]()







