ƘARSHEN tika-tika tik! Jiran da ake ta yi na ganin auren fitaccen mawaƙi, furodusa kuma jarumi Shu’aibu Ahmed Abbas, wanda aka fi sani da Lilin Baba, da fitacciyar jaruma Rahab Saleh Ahmed, wadda aka fi sani da Ummi Rahab, ya zo ƙarshe, domin kuwa yau saura kwana 14 a ɗaura auren su.
Za a ɗaura auren nasu da ƙarfe 11:00 na safe a ranar Asabar, 18 ga Yuni, 2022 a Tudun Murtala, NEPA Office, hannun riga da gidan Bala Kasa, Tudun Murtala, Jihar Kano.
Duk da yake Lilin Baba da Ummi ba su ɗauki tsawon lokaci su na soyayya ba, amma babu wanda bai san da soyayyar su ba saboda irin nuna wa junan su so da ƙaunar juna a soshiyal midiya.
A kai a kai sun yi ta jefa kalaman soyayya a kan junan su. Na baya-bayan nan shi ne rubutun da jarumar ta yi da Turanci a daren jiya, inda ta ce: “Lakal Hamd Ya Allah for giving me such an amazing husband, the best I could ever have. Ya Allah protect him, guide him and increase him in faith, health and wealth. Ya Allah grant us khair in our ever living ya Allah. This is my Jannah.”
Ma’ana: “Ya Allah ina gode maka da ka ba ni irin wannan miji mai ban-sha’awa, wanda babu wani kamar sa da zan iya samu. Ya Allah ka kare shi, ka yi masa jagora, kuma ka yalwata shi da imani da lafiya da dukiya. Ya Allah ka ba mu alheri a zaman auren mu ya Allah. Wannan shi ne Aljanna ta.”
Daga nan ta rufe da taken auren su a soshiyal midiya, wato @shurab_2022.
Ɗimbin masoyan su sun amsa mata da amin tare da yi masu fatan alheri.
Lilin Baba da Ummi dai sun fara soyayya ne a daidai lokacin da jarumar ta rabu da tsohon ubangidan ta, Adam A. Zango, a wani yanayi na ɓatawa tare da tozarci. A lokacin har Lilin Baba ya yi bidiyon wasu waƙoƙin sa da ita, sannan ya yi fim ɗin sa mai dogon zango, wato ‘Wuff’, da ita a matsayin jarumar shirin.
Daga nan Ummi ta daina aikin kowa a industiri in ba na sahibin nata ba.
Yanzu kam sauran ƙiris ta zama tasa.
![]()







