• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Wednesday, May 13, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Ni ɗan asalin Kano ne: Amsar Nuhu Abdullahi ga masu yi masa gorin asali

by DAGA MUHAMMAD LAWAN RANO
November 17, 2021
in Labarai
0
Nuhu Abdullahi

Nuhu Abdullahi

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

* Ya baje-kolin takardun sa a Facebook

TAURARON Kannywood Nuhu Abdullahi ya maida wa masu yi yarfen asali martani, inda ya nuna cewa shi cikakken ɗan Kano ne.

Don tabbatar da hakan, Nuhu ya baje-kolin takardun sa na makaranta da shaidar haihuwa.

Takardun sun haɗa da na shaidar makarantun firamare da sakandare da ya yi.

Nuhu, wanda ake yi wa laƙabi da Mahmoud, ya yi haka ne bayan wani mutum ya yi masa gorin asali sakamakon wata hira da sashen Hausa na BBC su ka yi da shi a shirin su na ‘Daga Bakin Mai Ita’.

Sun yi hira da Nuhu ne dangane da rayuwar sa da sana’ar sa ta fim. 

Nuhu Abdullahi a matsayin ɗan makaranta a Kwalejin Gwamnati ta Kano

Tun da farko mutumin, mai suna Ishaƙa Usman Wali, ya yi wa jarumin ƙorafi a kan yadda wai ya ke gudun asalin sa a dalilin ɗaukakar da ya samu.

A cikin buɗaɗɗiyar wasiƙar ta Ishaƙa, wadda ta bazu a soshiyal midiya, ya ce masa, “Na yi matuƙar mamaki irin yadda na kalli hirar ka da BBC Hausa a shirin su na ‘Daga Bakin Mai Ita’, inda su ka so su ji tarihin ka, kai kuma sai ka nuna masu cewa an haife ka a garin Kano, ka yi firamare da sakandare duk a Jihar Kano. 

“Hakika na ji babu daɗi sakamakon irin yadda na ga ka juya wa ƙauyen ku baya saboda yanzu rayuwar ka ta ci gaba kuma na yi mamaki matuƙa.”

Da alama, wannan iƙirarin ya fusata jarumin a yau, mako guda bayan an yi hirar da shi, har ya baje-kolin takardun sa da ke nuna cewa shi haifaffen unguwar Kawo ne da ke yankin Ƙaramar Hukumar Nassarawa a birnin Kano.

Sai dai kuma mujallar Fim ta lura da cewa jarumin ya yi wuf ya goge takardun da ya wallafa masu nuna asalin shi haifaffen Kano ne. 

Sai dai daga baya jarumin ya yi wata gajeruwar nasiha ga matasa a kan su guje wa munanan halaye tare da ƙaurace wa dukkan abin da ka iya ɓata masu lokaci.

Ya ce, “Salam, kira na ga ‘yan’uwa na matasa mu maida hankali wurin ciyar da kan mu da wasun mu gaba, mu daina ɓata lokaci a kan abin da zai ɓata mana lokaci wanda bai da amfani. 

“A ‘yan shekaru na na samu cigaban da ko a mafarki ban yi zaton zan samu ba, amma Allah cikin ikon sa ya sa na samu. 

“Mu zama masu jajircewa a kan abin da ya ke gaskiya da kuma amana. Mu kuma guji ƙarya da sharri da hassada da ƙyashi, Allah sai ya taimake mu.

“Wanda ya yi min waccan ƙaryar na yafe masa, kuma Allah ya shiryar da shi, amin.”

Gorin asali dai ba baƙon abu ba ne ga mutanen da su ka yi shuhura a wani ɓangare na rayuwa. Sai dai kuma a mafi yawan lokuta a birnin Kano a kan yi wa mutum gorin cewa ba ɗan asalin garin ba ne, inda a kan jefe shi da kalmar ‘baƙo’ ne ko kuma a danganta da shi da wata ƙabila ta daban.

Loading

Tags: asaliBBC Hausahausa filmsIshaka Usman WaliKannywoodKanoNuhu Abdullahi
Previous Post

Cewar Umar Gombe game da rasuwar mahaifin sa: ‘Ina alfahari da shi sosai’

Next Post

Yadda aka kashe jarumi Sani SK da labarin ƙarya a soshiyal midiya

Related Posts

Rasuwar dattijon Kannywood, Nura Shareef, ta girgiza ‘yan fim
Labarai

Rasuwar dattijon Kannywood, Nura Shareef, ta girgiza ‘yan fim

February 22, 2026
Daraktar fim ta ƙi karɓar awad saboda kisan gillar da Isra’ila take yi a Gaza
Labarai

Daraktar fim ta ƙi karɓar awad saboda kisan gillar da Isra’ila take yi a Gaza

February 21, 2026
Fitaccen furodusa Kunle Afolayan ya yi haɗin gwiwa da Jamhuriyar Benin kan shirya finafinai
Labarai

Fitaccen furodusa Kunle Afolayan ya yi haɗin gwiwa da Jamhuriyar Benin kan shirya finafinai

February 19, 2026
An naɗa Farfesa Tengya matsayin sabon shugaban Cibiyar Koyon Finafinai ta Ƙasa
Labarai

An naɗa Farfesa Tengya matsayin sabon shugaban Cibiyar Koyon Finafinai ta Ƙasa

February 15, 2026
Alƙali ya ci Samha Inuwa tara ko ta je kurkuku wata 6
Labarai

Alƙali ya ci Samha Inuwa tara ko ta je kurkuku wata 6

February 13, 2026
Hukumar EFCC ta kama jarumar Kannywood, Samha Inuwa, saboda goge majina da takardun naira
Labarai

Hukumar EFCC ta kama jarumar Kannywood, Samha Inuwa, saboda goge majina da takardun naira

February 3, 2026
Next Post
Sani Garba SK a asibiti, cikin wani bidiyo inda ya ke roƙon kuɗin magani

Yadda aka kashe jarumi Sani SK da labarin ƙarya a soshiyal midiya

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!