‘YAN dandatsa (hackers) a jiya sun ƙara samun nasarar ƙwace wa Adam A. Zango shafin sa na Instagram, wanda wannan shi ne karo na uku da su ka yi masa haka.
Wani mai lura da al’amuran Kannywood ya faɗa wa mujallar Fim cewa babu shakka sace shafin zai illata yunƙurin da fitaccen jarumin ya ke yi na tallata sabon fim ɗin sa mai dogon zango na ‘Farin Wata Sha Kallo’.
Zango, wanda kuma fitaccen mawaƙi ne, ya fara shiga wannan tsaka-mai-wuya ne tun daga lokacin da ɓarayin intanet masu kutse su ka fara ƙwace masa shafin Instagram mai ɗauke da mabiya sama da miliyan ɗaya da dubu ɗari takwas (1.8m).
Bayan an sace shafin nasa a wancan lokacin, jarumin ya yi iyakacin ƙoƙarin sa don ganin an dawo masa da shi, amma abin ya faskara. Wannan dalilin ya sa ya buɗe sabon shafi, amma ba a kwana biyu ba su ka sake ƙwace shi.
A lokacin, har Zango ya ce ya haƙura da buɗe shafi a Instagram, domin ya na da yaƙinin cewa magabtan sa ne su ka taso shi a gaba.
Daga baya kuma, bisa shawara tare da damuwar makusantan sa da masoyan sa, sai ya sake buɗe wani shafin mai suna @officially_a_zango.
Shafin ya samu sama da mabiya 82,000 ya zuwa jiya Asabar, 21 ga Agusta, 2021, lokacin da aka ƙwace shi.
Wasu da dama har sun fara tunanin jarumin ya fara bulokin ɗin mutanen da bai aminta da su ba ne, sai daga baya aka gane ashe an sake ƙwace sabon shafin nasa ne.
Ɗaya daga cikin yaran Zango, Umar Bigshow, shi ne ya bada sanarwar sace shafin da aka yi, inda ya tura saƙon hoton shafin jarumin ɗauke da jan rubutu cewa ‘Hacked’, daga ƙasa kuma ya rubuta, “Allah ya fi ku.”
Al’amarin ya baƙanta wa masoyan Zango rai matuƙa, musamman a daidai wannan lokaci da ya ke amfani da Instagram wajen tallata fim ɗin sa na ‘Farin Wata Sha Kallo’.
Mutane da dama na mamakin yadda irin wannan abu ya ke faruwa ga babban manishaɗanci kamar Zango amma ya kasa shawo kan matsalar. Akwai ƙananan jarumai da mawaƙa da ma sauran jama’a da irin haka na faruwa da su, amma kuma cikin ƙanƙanen lokaci su ke samun nasarar dawo masu da shafukan su.
A shekarun baya, ɓarayin intanet sun taɓa yin kutse a shafin Facebook na Ali Nuhu, sai nan da nan jarumin ya biya wani ɗan ƙasar Indiya kuɗi, ya samu nasarar dawo masa da shafin nasa. Wannan dalilin ne ya sa Alin ya koma amfani da sunan “Ali Nuhu Mohammed” a Facebook.
To ko shi ma Adam A. Zango zai yi irin wannan tunanin na Ali Nuhu don ya samu gyara wannan matsalar da ya ke fuskanta? Ko kuma daga wannan sabon harin da aka kai masa zai haƙura ne da yin Instagram gaba ɗaya? Za mu gani.
![]()







