A RANAR Juma’a da ta gabata aka ɗaura auren tsohuwar jarumar Kannywood, Hajiya Sadiya Muhammad Tukur, wadda aka fi sani da Sadiya Gyale.
An ɗaura auren ta da sahibin ta, Alhaji Mustapha Umar, da misalin ƙarfe 2:00 na rana, bayan an idar da sallar Juma’a a masallacin Juma’a na unguwar Ja’en da ke Sharaɗa Phase 3.
Wasu daga cikin ‘yan Kannywood da su ka halarci ɗaurin auren sun haɗa da Malam Hussaini Sule Ƙoƙi, Baballe Hayatu da Alhaji Ibrahim Nasir.
Bayan ɗaurin auren an yi walima a gidan su amarya da ke nan Sharaɗa Phase 3, inda aka ci, aka sha.
Ango da tawagar sa sun halarci walimar, sai kuma Malam Hussaini Sule Ƙoƙi da Alhaji Ibrahim Nasir, Ɗanɗa Umar Maibiredi, Sadiq Ado da sauran mahalarta ɗaurin auren.


Mata ‘yan fim da su ka halarci bikin sun haɗa da Samira Ahmad, Hadiza Kabara, Fauziyya Sani (Maikyau), Fati Baffa Fagge, Maijidda Ibrahim, Hadiza Maikano, Fati Sulaiman da Maryam Jankunne.
Washegari Asabar, amarya ta tare a gidan mijin ta a Kaduna.
Allah ya ba su zaman lafiya da zuri’a ɗayyiba.




![]()







