ALLAH ya albarkaci tsohuwar fitacciyar jarumar Kannywood, Hadiza Maina, da samun ‘ya mace.
Hadiza ta haihu ne a ranar Talata, 13 ga Satumba, 2022, da misalin ƙarfe 7:00 na yamma a wani asibiti mai suna Ashmed da ke GRA, Zariya, Jihar Kaduna.
A jiya Talata aka raɗa wa jaririyar suna Habiba, wanda sunan mahaifiyar maijegon ne. Don haka za a riƙa kiran ta da Hibba.

An yi taron sunan ne a gidan mijin ta, Alhaji Lawandi Musa, da ke unguwar Muciya, Babban Titi, Sabon Gari, Zariya.
‘Yan fim mata waɗanda su ka halarci taron sunan sun haɗa da Ɗayyaba Ishaq, Ruƙayya Usman, A’isha B. Umar da Fati JJ.
Hadiza, wadda fitacciya ce a harkar fim a Kaduna, ta yi aure ne a ranar 4 ga Afrilu, 2009.

Ta shaida wa mujallar Fim cewa wannan haihuwa da ta yi ita ce ta uku, amma wannan ce ta tsaya, sauran biyun duk sun koma.
Allah ya raya Habiba, ya albarkaci rayuwar ta, amin.
![]()







