HAƊAƊƊIYAR Ƙungiyar Masu Shirya ta Nijeriya (MOPPAN) ta kira taron shekara na shugabannin ta na ƙasa na jihohi da sakatarorin su.
Sanarwar kiran taron, wadda kakakin ƙungiyar, Malam Al-Amin Ciroma, ne ya rattaba wa hannu, ta ce: “Bayan dogon nazari da tsare-tsare, kusan tun daga ƙarshen shekarar 2022, Haɗaɗɗiyar Ƙungiyar Masu Harkar Fim ta Ƙasa, MOPPAN, yanzu ta cimma matsayar gayyatar dukkannin shugabannin ta na ƙasa da kuma shugabannin jihohi da sakatarorin su zuwa taron ta na wakilai na shekara, wato ‘Annual Delegates’ Conference’.”
Ya ce za a gudanar da taron ne a ranar Asabar, 10 ga Yuni, 2023 da misalin ƙarfe 2:00 na rana, a ɗakin taro na Kannywood TV da ke kan Titin Muhammadu Buhari, Tudun Yola, cikon birnin Kano.
To, Allah ya ba da ikon halarta, amin summa amin.
![]()







