FURODUSA a masana’antar Kannywood, Hajiya Fatima Ibrahim Ahmed, wadda aka fi sani da Fatima Lamaj, ta zama sabuwar shugabar ƙungiyar Arewa Film Makers Association of Nigeria (AFMAN), reshen Jihar Kaduna.
Naɗin nata na ƙunshe ne cikin takardar da Sakatare-Janar na AFMAN na Ƙasa, Alhaji Sani Suke Katsina, ya sanya wa hannu.
Bisa ga takardar, wa’adin shugabancin Lamaj zai fara ne daga ranar 19 ga Yuni, 2026, zuwa ranar 19 ga Yuni, 2027, kamar yadda kundin tsarin mulki, dokoki da ƙa’idojin ƙungiyar suka tanada.
Majalisar zartarwa ta AFMAN ta bayyana cewa an ba ta wannan muƙami ne bisa la’akari da ƙwarewar ta da gogewar ta, tare da nuna cikakken yaƙinin cewa za ta gudanar da jagoranci nagari da zai ciyar da ƙungiyar gaba.
A matsayin ta na shugabar reshen Kaduna, za ta jagoranci ayyukan AFMAN a jihar, ta ƙarfafa haɗin kai tsakanin mambobi, ta bunƙasa manufofin ƙungiyar, tare da tabbatar da cewa ana gudanar da harkokin reshen bisa tanade-tanaden da umurnin sakatariyar AFMAN ta ƙasa.
Mujallar Fim ta ruwaito cewa shugabannin ƙungiyar sun taya Fatima Lamaj murnar wannan naɗi, tare da yi mata fatan Allah ya ba ta hikima da nasara wajen sauke nauyin da aka ɗora mata.
Lamaj dai ta taɓa zama Shugabar ƙungiyar MOPPAN reshen Jihar Kaduna.
![]()







